BBC News, Hausa - Labaran Duniya
Babban Labari
Peter Obi ya buƙaci ƴanbindiga su saki ɗaliban da suka sace
Wannan shafi ne da ke kawo muku labarai kan abubuwan da ke faruwa tsakanin Iran da Amurka da Isra'ila da kuma sauran muhimman abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Laraba 03/06/2026.
BBC ta gano yadda Shell ke fitar da ɗanyen mai duk da shaidar gurɓata muhalli a Najeriya
Wasu takardu da BBC ta samu sun nuna cewa Kamfanin Mai na Shell na Birtaniya ya ci gaba da aikin haƙar mai a Najeriya tsawon shekaru duk da cewa kamfanin ya san cewa yana gurɓata muhalli.
An kama surukar da ake zargi da taimakawa wajen kashe matar ɗanta
Iyayen matar da aka kashe, Twisha Sharma da ƴan'uwanta sun yi zargin cewa mijinta da mahaifiyarsa ne suka azabtar da marigayiyar har suka kashe ta a kan kuɗin sadaki.
Me ya rage wa Arsenal bayan gaza ɗaukar Champions League?
Bayan da ta lashe Premier League na farko bayan shekara 22, babban jami'in labaran ƙwallon ƙafa na BBC, Sami Mokbel, ya yi nazari kan jerin abubuwan da Arsenal ke bukatar yi gabanin kaka mai zuwa.
'Trump na son a kawo ƙarshen yaƙi amma Iran ta ƙi bayar da haɗin kai'
Bayan shan matsai daga ƙawayen Amurka na yankin Gulf, Trump na neman a cimma yarjejeniya amma na son sai an biya ta diyya.
Me Inec za ta yi kan ƴantakara fiye da ɗaya da jam'iyyun adawa suka tsayar?
Wa'adin da hukumar zaɓen Najeriya ta sanya ga jam'iyyun siyasa su kammala gudanar da zaɓen cikin gida sannan kuma su miƙa sunayen ƴan takararsu da za su tsaya musu takarar zaɓen 2027, ya wuce.
Ko gwamnatin jihar Kano za ta iya kawar da matsalar daba?
Kwamishinan shari'a na jihar ya ce: "Za mu tabbatar da cewa idan har aka kawo mana masu laifi musamman daba, doka ta yi halinta ko da kuwa jami'in gwamnati ne, ba sani ba sabo."
Me ya sa Isra'ila da Hezbollah ke son kame ganuwa mai shekara 900?
Wani hoton bidiyo da sojojin Isra'ila suka saki ya nuna wasu dakarun sojin ƙasar na ratsawa ta cikin wata tsohuwar ganuwa da ke kan tsauni wadda aka gina tun zamanin da
Nau'in ciwon suga da ke kama siraran mutane
An gano cewa ciwon suga nau'in Type 5 na faruwa ne sanadiyyar tsawon lokaci ba tare da samun abinci mai gina jiki ba, musamman idan mutum ba ya samun ingantaccen abinci na tsawon lokaci ko kuma a lokacin girma. Sai dai har yanzu masana ba su kammala amincewa ko da gaske ciwon na wanzuwa ba ko a'a'.
Shirye-shiryenmu
Saurari na gaba, Shirin Safe, 05:29, 4 Yuni 2026, Tsawon lokaci 30,00
Shiri ne na minti 30 wanda ya kunshi labaru da rahotanni daga sassa daban na duniya.
Saurari, Shirin Yamma, 19:29, 3 Yuni 2026, Tsawon lokaci 30,00
Shiri ne na minti 30 wanda ya kunshi labaru da rahotanni daga sassa daban-daban na duniya.
Saurari, Shirin Rana, 13:59, 3 Yuni 2026, Tsawon lokaci 30,00
Shiri ne na minti 30 wanda ya kunshi labaru da rahotanni daga sassa daban-daban na duniya.
Saurari, Shirin Hantsi, 06:30, 3 Yuni 2026, Tsawon lokaci 29,30
Shiri ne na minti 30 wanda ya kunshi labaru da rahotanni daga sassa daban na duniya.
Wasanni
Su wane ne ƴankwallon da suka fi arziki a duniya?
Mujallar Fobes ta ruwaito cewa Ronaldo na da arzikinsa ya kai dala biliyan 1.4 .
Duk abin da ya kamata ku sani kan Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026
Wani babban sauyi da aka samu a gasar ta 2026 shi ne ƙarin yawan ƙasashen da za su fafata zuwa 48.
Man City da Chelsea na son Cambiaso, Barca za ta riƙe Rashford
Manchester City da Chelsea na son ɗan baya na gefe na Juventus Andrea Cambiaso, kamar yadda ita ma Barcelona wadda ke son saye Rashford ke sa ido a kan Cambiason.
KAI TSAYE, Bellingham ne zai sa wa Ingila lamba 10 a gasar kofin duniya
Wannan shafi ne da zai ke kawo muku labaran wasannin BBC Hausa daga Litinin 01 zuwa Lahadi 07 ga watan Yunin 2026.
Yadda aka caccaka wa mutane wuka bayan bikin murnar ɗaukar kofin Arsenal
Ƴansandan Metropolitan sun ce an kama mutane 24 a ranar Lahadi a kan ko kusa da hanyar da aka yi bikin.
Tashar WhatsApp ta BBC Hausa
A wannan shafin za ku samu labarai daga ƙasashen Afrika da kuma sauran sassan duniya da ɗumi-ɗuminsu domin masu bibiyar mu a WhatsApp.
Kuna son tattalin datarku?
Shiga shafinmu na labarai maras hoto domin rage zuƙar data
Labarai da Rahotanni Na Musamman
Manyan sojojin Najeriya biyu da ƴanbidiga suka sace
Sace babban jami'in sojin Najeriya da ya yi murabus, tare da maidakinsa a jihar Katsina da ke arewa maso yammacin Najeriya, ya ƙara jefa fargaba a zuciyar ƴan Najeriya dangane da tsaro.
Sansanonin sojin Amurka 20 da Iran ta lalata
Masana sun shaida wa sashen BBC mai bincike na BBC Verify cewa hare-haren Iran sun yi ɓarna fiye da abin da ya bayyana ga al'umma.
Yadda rikici ya kunno kai a APC a Jigawa
Jam'iyyar ta ce ta dakatar da ɗanmajalisar da ke wakiltar Hadejia da Auyo da Kafin Hausa, a majalisar wakilai ta tarayya, Usman Kamfani Auyo da wasu mutum shida, saboda zargin barazanar yi mata zagon-ƙasa a zaɓe mai zuwa, saboda rashin samun takarar da ɗanmajalisar ya yi.
Iran ta ce ta kai hare-hare kan sansanonin sojin Amurka
Wannan shafi ne da ke kawo muku labarai kan yaƙin Iran da kuma abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Litinin 01/06/2026.
Me ya sa malaman makaranta ke zanga-zanga a jihar Oyo?
Ɗaruruwan malaman makaranta da iyaye da ƙungiyoyin matasa ne suka fantsama kan titunan jihar Oyo domin yin zanga-zanga kan abin da suka kira rashin taɓuka komai daga gwamnati don ceto ɗalibai da wasu malamansu da ƴanbindiga suka sace makwanni biyu da suka gabata.
'Abin da ya sa kakana ya shiga yaƙin Biyafara'
Wani mashiryin fim ɗan Najeriya Meji Alabi ya bayar da umarni wajen haɗa wani muhimmin rahoto na musamman na sashen binciken ƙwaƙwaf na BBC Africa Eye kan yaƙin basasar Najeriya.
Ƴan takaran da za su tsaya wa manyan jam'iyyun Najeriya a zaɓen shugaban ƙasa na 2027
Tuni shirye-shiryen zaben suka kankama, inda 'yantakara suka fara tallata kan su domin neman kuri'a.
Yadda ‘yan bindiga suka sace tsohon babban sojan Najeriya da matarsa a Katsina
Ci gaba da irin wannan garkuwa da mutane na nuna karuwar wannan matsala ta rashin tsaro wadda ta addabi arewa maso yammacin Najeriya.
Zafin kaye ne ya sa wasu ke zargin rashin adalci a tsayar da ni takara - MA Abubakar
Tsohon gwamnan jihar Bauchi, kuma dan takarar gwamnan jihar a zaben 2027 da ke tafe Barista Muhammad Abdullahi Abubakar, ya musanta zargin da wasu da suka nemi takarar da shi ke yi na cewa ba a gudanar da zaben cikin gida ba aka tsayar da shi takara.
Ba za mu amince da duk wata yarjejeniya ba sai mun tabbatar za a biya mu diyya - Iran
Wannan shafi ne da kawo muku muhimman bayanan dangane da wainar da ake toyawa a Najeriya da sassan duniya na ranar Lahadi 31 ga watan Mayun 2026.
Ina Iran ta ɓoye sinadarin Uranium ɗinta na haɗa nukilya?
Shin me ya sa Iran ta adana sinadarin, kuma ina makomar sinadarin?
Yadda takara guda shida da Atiku ya yi a baya suka kasance
A yanzu ya sake samun tikitin takara, wanda wannan ne karo na bakwai da yake takara.
KAI TSAYE - Labaran BBC Hausa
Saurari labaran BBC Hausa Kai Tsaye Litinin zuwa Juma’a da karfe 0530, 0630, 1400 da 1930 GMT, sai kuma Asabar da Lahadi da karfe 0530, 0630 da 1930 GMT.






























































