Yaƙin Iran da abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 01/06/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku labarai kan yaƙin Iran da kuma abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Litinin 01/06/2026.

  • xxx
  • xxx
  • xxx
  • xxx
  • xxx
  • Sadis Buba
  • Pantami
  • xxx
  • Nafiu Gombe
  • Mace da ƴarta mai lalaurar Autism
  • wata mata
  • BBC reporter

Rahoto kai-tsaye

Nabeela Mukhtar Uba, A'isha Babangida, Haruna Kakangi

  1. Sabuwar cukumurɗar siyasa ta taso a jihar Ribas

    Siminalayi Fubara

    Asalin hoton, Sir Siminalayi Fubara/FACEBOOK

    Bayanan hoto, Governor Siminalayi Fubara

    Shugabancin jam'iyyar APC da kotu ta mayar kan iko a jihar Ribas ya ayyana duk zaɓen fitar da gwani na jam'iyyar a jihar ta kudu maso kudancin Najeriya, a matsayin haramtacce da ya saɓa wa doka.

    Zaɓukan su ne dai suka fito da Kingsley Chinda - wani na-hannun daman Nyesom Wike, ministan Abuja, babban birnin Najeriya - a matsayin ɗan takarar gwamna na APC bayan Siminalayi Fubara, gwamna mai ci ya janye.

    Sauran abokan tafiyar Wike ne suka zama 'yan takarar APC na zaɓuka masu zuwa a guraben majalisar tarayya da majalisar dokokin jihar Ribas.

    Jaridar Daily Trust ta ruwaito yadda Mai shari'a Elfreida Oluwayemisi Williams-Dawodu ta Kotun Ɗaukaka Ƙara a ranar Juma'a, ta tabbatar da hukuncin Babbar Kotun Jihar RIbas wanda ya soke tarukan jam'iyyar APC da suka samar da shugabancin Cif Tony Okocha.

    A wata sanarwa da ya fitar ranar Litinin, Darlinton Nwauju mai magana da yawun shugabancin APC da kotu ta mayar kan iko a ƙarƙashin jagorancin Emeka Beke, ya ce dogaro da hukuncin kotun, dukkan masu neman takara da wakilai da harkokin sadarwa da takardu ciki har da shawarwarin da aka cimma a madadin jam'iyyar APC reshen Jihar Ribas daga ranar 20 ga watan Disamban 2024 zuwa 29 ga watan Mayun 2026, ba su da wani tasiri a jam'iyyance.

  2. Faransa ta kama jirgin dakon mai na Rasha

    Faransa ta ce ta kama wani jirgin ruwan dakon mai na Rasha da aka sanya wa takunkumi a kan tekun Atlantika, tare da taimakon Birtaniya da kuma sauran ƙawayenta.

    Moscow ta soki ƙwace jirginta, inda ta ce hakan abu ne da ya haramta, kuma tamkar fashin teku ne.

    Kakakin fadar Kremlin Dmitry Peskov ya ce Rasha na ɗaukar matakai domin tabbatar da tsaron jirgin ruwan na dakon mai.

    Jirgin, mai suna Tagor, na ɗauke da rijistar ƙasar Kamaru.

    Wakilin BBC ya ce Shugaban Faransa Emmanuel Macron ya ce ba za a lamunci yadda jirage irin waɗannan ke karya takunkuman da aka sanya musu ba, kuma su riƙa samar wa Rasha kuɗin da za ta cigaba da yaƙi da Ukraine.

  3. An ƙaddamar da rundunar tsaron Mashigin Tekun Guinea ta haɗin gwiwa

    Nigerian Navy

    Asalin hoton, Nigerian Navy

    Bayanan hoto, Sojojin ruwan Najeriya suna fareti a bikin cikar rundunar shekara 70 da kafuwa

    Najeriya ta ƙaddamar da rundunar haɗin gwiwa mai tsaron Mashigin Tekun Guinea da goyon bayan Tarayyar Afirka da nufin ƙarfafa tsaron teku a faɗin Afirka ta Yamma.

    Wata sanarwa da rundunar sojojin ruwan Najeriya ta fitar na cewa da hedkwatarta a Lagos, sabuwar rundunar ta haɗa dakarun sojojin ruwa daga Najeriya da Ghana da Liberia da Sierra Leone da Gambiya da kuma ƙasar Aburi Kwas don haɗa gwiwa kan ayyukan sintiri da shirin yaƙi kan ƙungiyoyin tsara laifuka na a tsakanin ƙasashe ciki har da 'yan fashin teku a faɗin Mashigar Tekun Guinea mai girman kimanin kilomita 6,000.

    Da yake jawabi yayin ƙaddamar da rundunar, Shugaba Bola Tinubu ya ce matakin wata manuniya ƙarara na ƙudurin ɗaukacin ƙasashen wajen ƙarfafa ayyukan haɗin gwiwa cikin harkokin gudanar da teku.

    Nigerian Navy parade

    Asalin hoton, Nigerian Navy

    Bayanan hoto, Sojojin ruwan Najeriya suna fareti

    Sanarwar ta ce kafa sabuwar rundunar haɗin gwiwar tsaron Mashigin Tekun Guinea, wani martani ne kai tsaye ga damuwar da kamfanonin inshorar sufurin teku na duniya da masu jigilar kaya da hukumomin kula da tashoshin ruwa, suka dade suna nunawa, bayan sun sha bayyana Mashigin Tekun Guinea a matsayin ɗaya daga cikin yankunan teku mafi hatsari a duniya.

    Babban Hafsan rundunar sojojin ruwan Najeriya, Vice Admiral Idi Abbas ya ce sabuwar rundunar za ta tashi tsaye wajen yaƙi da barazanar da take tasowa a teku sannan za ta tallafawa ayyukan jin ƙai da tabbatar da zaman lafiya a Afirka ta Yamma.

  4. Sabon firaministan Hungary zai samar da dokar tsige shugaban ƙasa

    ..

    Asalin hoton, Getty Images

    Sabon Firaiministan Hungary, Peter Magyar, ya ce gwamnatinsa za ta yi wa kundin tsarin mulkin ƙasar gyaran fuska domin ya bayar da damar tsige shugaban ƙasar idan bai ajiye aiki ba.

    Ya ce ina ganin wannan aikin zai iya ɗaukar mu aƙalla wata guda, za mu yi ƙoƙari mu amince da sabbin dokokin da muke buƙata cikin ƙanƙanin lokaci.

    Wannan wani yunƙuri ne na ganin ya kawar da dukkanin jami'an gwamnatin da wanda ya gabace shi, mai biye wa ra'ayin jama'a Viktor Orban ya naɗa.

    Shugaba Tamas Sulyok, wanda ke cikin shekararsa ta biyu kan mulki, cikin wa'adin shekara biyar, ya ƙi amincewa ya sauka.

    An zaɓi mista Magyar ne bayan gagarumar nasarar da ya yi a watan Afrilu, inda ya sha alwashin dawo da tsarin gwamnati na jan linzami da kuma daidaito.

  5. An dakatar da zaɓe a wasu sassan Habasha saboda rashin tsaro

    A woman casting a vote

    Asalin hoton, AFP via Getty Images

    Bayanan hoto, Wannan ne zaɓe na bakwai a Habasha tun bayan faɗuwar mulkin sojoji a 1991

    An dakatar da kaɗa ƙuri'a a babban zaɓen ƙasar Habasha cikin yankunan Oromia da Amhara saboda dalilai na tsaro. yayin da aka shaida dogayen layukan masu zaɓe a wasu sassa, kamar yadda shugaban hukumar zaɓen ƙasar Melatwork Hailu ya bayyana

    Rikici a wasu yankunan ƙasar ta biyu mafi yawan jama'a a Afirka tun tuni na nufin cewa da yawan 'yan Habasha ba za su samu damar shiga zaɓen ba, wanda shi ne na bakwai bayan kawo ƙarshen zamanin mulkin sojoji masu ra'ayin Markisanci a 1991.

    Alal haƙiƙa ma, gaba ɗayan yankin Tigray, wanda ke ƙoƙarin farfaɗowa daga wani yaƙin basasar da aka kawo ƙarshe a 2022 kwata-kwata an ware shi daga zaɓen.

    Duka-duka, a yayin da aka samar da tasoshin zaɓe fiye da 50,000 amma wasu 143 sun gaza buɗewa saboda matsalar rashin tsaro.

    Yayin kaɗa ƙuri'arsa, Firaminista Abiy Ahmed wanda ke kan mulki tun a shekara ta 2018, ya yaba wa ci gaban da Habasha ta samu tun bayan kawo ƙarshen mulkin sojoji 'yan kama-karya.

  6. Iran ta ce ta kai hare-hare kan sansanin sojin Amurka

    ..

    Asalin hoton, Getty Images

    Iran ta ce ta kai hari kan wani sansanin sojin saman Amurka, bayan da Amurkar ta ƙaddamar da sabbin hare hare kan Iran a kwanakin ƙarshen mako.

    Dakarun juyin juya halin Iran ba su bayyana inda sansanin yake ba, amma Kuwait ta ce na'urorin kare sararin samaniyarta sun kakkaɓo jirage marasa matuƙa da makamai masu linzami.

    Amurka na da wani sansanin soji mai muhimmanci a Kuwait.

    Washington ta kai hare hare da dama kan wuraren samar da jirage marasa matuƙa na Iran a birnin Goruk da ke Hormozgan, da kuma tsibirin Qeshm.

  7. Hare-haren Isra'ila a Lebanon na barazanar ruguza yarjejeniyar tsagaita wuta - Iran

    soldiers standing next to a civilan vehicle

    Asalin hoton, Reuters

    Bayanan hoto, Iyalai da yawa na tserewa daga unguwannin wajen Beirut bayan sojojin Isra'ila sun cewa mazauna su fice.

    Iran ta yi gargaɗin cewa hare-haren Isra'ila a kan Hezbollah a Lebanon na barazana ga yarjejeniyar tsagaita wutar ƙasar da Amurka, firaminista Benjamin Netanyahu ya ba da umarnin kai hare-hare kan unguwannin fuskar kudu a wajen birnin Beirut.

    Ministan wajen Iran Abbas Aragchi ya ce yarjejeniya da Amurka "ƙarara tsagaita wuta ne da ya shafi dukkan fagen yaƙi, ciki har da Lebanon" kuma "keta yarjejeniyar ta fage guda, keta yarjejeniyar tsagaita wuta ce a dukkan fagagen yaƙi".

    Tun da farko, Firaminista Benjamin Netanyahu ya ce za a kai farmaki kan "wuraren 'yan ta'adda" a Dahieh domin mai da martani ga hare-haren jirage marasa matuƙi da rokoki kan fararen hula na Isra'ila da kuma sauran take yarjejeniyar tsagaita wutar da aka sanar a watan Afrilu wada ta gaza kawo ƙarshen kafsa faɗa..

    Can a wani wuri daban, kamfanin dillancin labaran Iran mai suna Tasnim ya ruwaito cewa hukumomin Tehran na iya dakatar da tattaunawar da ba ta kai tsaye ba da Amurka.

  8. Malaysia ta haramata wa ƴan ƙasa da shekara 16 shiga soshiyal midiya

    ..

    Asalin hoton, Getty Images

    Malaysia ta fara hana ƴan ƙasa da shekara 16 buɗe shafukan sada zumunta.

    Hukumar kula da harkokin sadarwa ta ƙasar ta ce dole ne shafuka kamar Fesbuk da Instagram da Tikok da YouTube su tantance shekaru kan bayanan gwamnati da aka bayar.

    Malaysia ta bi sahun ƙasashen da suka bijiro da matakai makamancin haka domin kare yara daga ganin abubuwan da ba su kamata ba a shafukan sada zumunta.

    Kamfanonin da suka ƙi bin matakin za su fuskanci tarar kusan dala miliyan biyu da rabi.

    Wakilin BBC ya ce za a soma tantance shekarun waɗanda suka riga suke amfani da shafukan domin aiwatar da dokar nan da watanni shida.

  9. Rundunar sojin ruwan Najeriya ta ƙaddamar da jiragen yaƙi uku

    Nigerian Navy vessel

    Asalin hoton, Nigerian Navy

    Bayanan hoto, Nigerian Navy vessel

    Shugaba Bola Tinubu na Najeriya ya ce rundunar sojojin ruwan ƙasar ta yi nasarar kakkaɓe ayyukan 'yan fashin teku da kuma gagarumar raguwar satar ɗanyen man fetur a tekunan Najeriya.

    Tinubu ya yi wannan jawabi ne ranar Litinin lokacin da yake ƙaddamar da Bitar Rundunonin Duniya na Sojin Ruwan Najeriya a gaɓar tekun Victoria Island, cikin Lagos

    Taron wani ɓangare ne na bikin cika shekara 70 da kafa rundunar sojin ruwan Najeriya, tun bayan ƙaddamar da ita ranar 1 ga watan Yunin 1956.

    Shugaba Tinubu ya yaba wa sojojin ruwan saboda ƙarfin aikin rundunar na zamani, inda ya nunar cewa sojojin ruwan Najeriya kai tsaye sun kare garuruwan gaɓar teku.

    A yayin bikin an ƙaddamar da jiragen sojojin ruwa guda uku waɗanda ta sanya wa sunayen NNS Mambila da NNS Gurara da kuma NNS Olobiri.

    Nigerian Navy vessels

    Asalin hoton, Nigerian Navy

    Bayanan hoto, Jiragen ruwan yaƙin Najeriya
  10. Babachir Lawal ya fita daga ADC

    Babachir Lawal

    Asalin hoton, OTHER

    Bayanan hoto, Babachir Lawal

    Tsohon Sakataren Gwamnatin Najeriya, Babachir Lawal ya yi murabus daga jam'iyyar ADC ta haɗakar 'yan adawa.

    Kafofin labarai a Najeriya sun ambato Babachir na bayyana fita daga ADC a cikin wata sanarwa mai ɗauke da kwanan watan Litinin 1 ga Yulin 2026.

    Tsohon Sakataren Gwamnatin ya yi zargin cewa kurakurai sun ɓata zaɓen fitar da gwani na jam'iyyar kuma an jirkita sakamakon zaɓen don ya fifita ɗan takarar shugaban ƙasa na ADC Atiku Abubakar da mutanen da suke goyon bayansa.

    Ya ce yadda aka gudanar da zaɓen fitar da gwanin ya nakasa ƙwarin gwiwar da ake da shi a tsarin dimokraɗiyyar cikin gida na jam'iyyar sannan ya yi tasiri ga shawararsa ta barin ADC.

    Babachir ya ce ba zai iya ci gaba da zama a jam'iyyar da in ji shi aka mayar da halastattun 'yan siyasan da suka yi nasara ba sannan aka maye gurbinsu da wasu shafaffu da mai.

    Ofishin yaɗa labaran tsohon mataimakin shugaban na Najeriya, Atiku Abubakar ya ce tsohon sakataren gwamnatin bai iya gabatar da shaida a kan zarge-zargen da ya yi ba.

    Ya ce zaɓukan fitar da ɗan takarar shugaban ƙasar na jam'iyyar ADC an gudanar da su a faɗin dubban mazaɓu da ke Najeriya inda ya samar da wani fayyataccen sakamakon da ya raba gardama.

  11. Za a rushe gidaje 26,000 a birnin Yamai na Nijar

    ..

    Asalin hoton, Elmastro TV

    A jamhuriyar Nijar, hukumomi a babban birnin ƙasar Yamai sun ƙaddamar da wani gagarumin aikin rusau a ranar Lahadin ƙarshen makon nan.

    Hakan dai na zuwa ne bayan cikar wa’adin da hukumomi suka bai wa mazauna unguwani huɗu da ke kewayen filin jirgin saman birnin wanda zai shafi sama da mutane dubu 26,000.

    Mahukuntan ƙasar ta Nijar sun bayyana yanayin tsaro a matsayin hujjarsu ta gudanar da wannan aiki.

    A watanni da suka gabata ne dai wasu ƴan bindiga da ake kyautata zaton ƴan Boko Haram suka kai hare-hare filin jirgin saman birnin na Yamai.

    Sai dai mazauna unguwannin sun nemi ƙarin lokaci don ficewa da kuma a biyan su diyya daidai da kuɗin da suka kashe wajen gina gidajen nasu.

  12. Ƙungiyar ƙwadago na son albashi mafi ƙanƙanta ya koma miliyan ɗaya

    ..

    Asalin hoton, Getty Images

    Ƙungiyar ƙwadago ta NLC a Najeriya ta yi watsi da tayin ƙarancin albashi na naira 100,000 da ƙungiyar gwamnonin ƙasar suka yi.

    Ƙungiyar ta ce idan aka yi duba da halin da ake ciki na tsadar rayuwa a ƙasar ya kamata a ƙalla a riƙa biyan ma'aikata mafi ƙarancin albashi na naira miliyan daya.

    Sakataren tsare-tsare na ƙungiyar Kwamared Nasir Kabir ya shaida wa BBC cewa idan har gwamnatin ta gaza yin abin da ya dace za su ɗauki mataki.

    A yanzu dai albashi mafi ƙaranci shi ne naira dubu 72,000.

  13. Majalisar dokokin Afirka ta Kudu na yunƙurin tsige Cyril Ramaphosa

    ..

    Asalin hoton, Getty Images

    Majalisar dokokin Afirka ta kudu ta fara yunƙurin tsige shugaban ƙasar, Cyril Ramaphosa kan abin kunyar da ya shafi badaƙalar sama da rabin dala miliyan daya da aka sace a gonarsa.

    Kwamitin da majalisar ta kafa domin gudanar da bincike kan zarge-zargen zai gudanar da zamansa na farko a ranar Litinin.

    Da ma dai ƴan ƙsar sun yi ta kiraye-kirayen shugaban da ya yi murabus.

    A shekarar 2022 ne wata kotu mai zaman kanta ta ce Ramaphosa zai amsa tambayoyi kan ɓarayin da suka saci tsabar kuɗi dala 580,000 da aka ɓoye a cikin kujera a gidansa da ke ƙauye.

    Satar dai ta janyo zargin cewa bai bayar da bahasin daga inda aka samo kuɗin ba. Shugaba Cyril Ramaphosa dai ya musanta yin wani abu da ya saɓa doka.

  14. Isra'ila ta bayar da umarnin kai hare-hare kan Hezbolla

    Isra'ila ta bada umarnin kai hare-hare kan Hezbollah a yankunan kudancin babban birnin Lebanon Beirut, matakin da ya sa mazauna babban birnin da dama tserewa.

    Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce sojojin ƙasar za su kai hare-hare ne kan abin da ya kira maɓoyar Hezbollah a yankin, a matsayin martanin harin da ƙungiyar ta kai kan farar hula a Isra'ila da kuma karya dokokin yarjejeniyar da aka cimma a watan Afrilu.

    Hezbollah ta yi ta harba rokoki da jirage marasa matuƙa arewacin Isra'ila, a yayin da su kuma dakarun Isra'ilar ke ci gaba da kutsawa kudancin Lebanon.

    Ƙungiyar Tarayyar Turai ta yi kira da Isra'ila da ta daina kai hare hare Lebanon, kuma ta mutunta ƴancinta.

  15. Ana zanga-zanga kan ƙaruwar kisan mata a Kenya

    ..

    Asalin hoton, Getty Images

    Ana zanga-zanga a Nairobi, babban birnin Kenya kan yadda ake samun ƙaruwar kisa da cin zarafin mata.

    Ɗaruruwan masu zanga-zangar su taru ɗauke da alluna da aka rubuta sunayen matan da aka ci zarafi ko ma aka kashe.

    An samu munanan kashe-kashe a Kenya har da kisan mawaƙiya kuma ƴar fafutuka da aka kashe tare da ƙona gawarta.

    Masu zanga-zangar na neman a ayyana kisan mata a matsayin matsalar da ta addabi ƙasar.

    Ƙungiyar kare haƙƙin bil adama ta Amnesty ta ce ana kai rahoton kisan mata aƙalla takwas duk mako.

  16. Zanga-zanga ta ɓarke a Oyo kan sace ɗaliban jihar

    Ɗaruruwan malaman makaranta da iyaye da ƙungiyoyin matasa sun fantsama titunan jihar Oyo domin yin zanga-zanga kan abin da suka kira rashin taɓuka komai daga gwamnati don ceto ɗalibai da wasu malamansu da ƴanbindiga suka sace makwanni biyu da suka gabata.

    Masu zanga-zangar ɗauke da alluna da ƙaton allo ɗauke da hotunan yara, wasu cikin tsoro wasu kuma na nuna jikinsu da tabbai.

    Wasu yara ƴan shekara 12 zuwa 15 suma sun bi sahun masu zanga-zangar.

    Zanga-zangar wani ɓangare ne na matakan malaman makarantun gwamnati karƙashin ƙungiyar malamai ta NUT na matsa wa gwamnati lamba ta kuɓutar da ɗalibai da malamansu da aka sace a watan da ya gabata.

  17. Gagarumar fashewa ta halaka mutum kusan 50 a Myanmar

    ..

    Asalin hoton, Shwe Phee Myay

    Aƙalla mutum 46 aka kashe, wasu da dama kuma suka ji rauni bayan wata fashewa a wani ƙauyen yankin Myanmar da ke hannun ƴanbindiga.

    Tawagar masu aikin ceto sun shaida wa BBC cewa daga cikin mamatan har da ƙananan yara shida har da wani ɗan shekara ɗaya.

    Fashewar ta lalata kusan gidaje 200 a Kaung Tat da wasu 100 da ke ƙauyen Pan Lone mai maƙwabtaka.

    Mayaƙa TNLA da ke riƙe da yankin kuma take yaƙi da gwamnatin soji ta ce abubuan fashewar da aka ajiye ne suka tashi, lamarin da ya janyo fashewar.

  18. DSS ta kama mutum biyar kan zargin hannu a sace ɗaliban Papiri

    ..

    Asalin hoton, Getty Images

    Hukumar tsaro ta farin kaya a Najeriya DSS ta kama mutum biyar ciki har da ƴan Nijar biyu da ake zargin suna kai wa ƴanbindiga makamai waɗanda a ranar 21 ga Nuwambar bara suka kai hari kan wata makaranta a ƙauyen Papiri da ke jihar Neja, inda suka sace ɗalibai kusan 300 da malamai.

    Gidan Talabijin na Channels ya ruwaito cewa daga cikin makaman da aka samu a hannun mutanen akwai tarin bindigogi da alburusai.

    Wasu majiyoyi da Channels ta ruwaito cewa Yusuf Mohammed da aka fi sani da Bature, wanda sunansa ke cikin jerin mambobin Boko Haram da ake ema ruwa a jallo sai Mubarak Ibrahim da aka kama a kan babbar hanyar Zaria zuwa Kaduna yayin da suke kan hanyarsu ta zuwa karɓar ƙunshin makamai da za su kai wa kwamandojinsu.

    Majiyar ta kuma ce wani samame da aka kai ya sa an kama Goni Ibrahim, da ya yi ƙaurin suna wajen safarar makamai daga Diffa a Jamhuriyar Nijar. Baya ga shi, an kuma kama Tukur Sani wanda suke aikin tare.

  19. Ana zanga-zanga a Kenya kan shirin buɗe cibiyar Ebola ta Amurka a ƙasar

    Zanga-zanga ta ɓarke a garin Nanyuki da ke Kenya game da shirin gina cibiyar killace masu Ebola ta Amurka a sansanin sojin sama na Laikipia.

    Mazauna garin sun yi tattaki inda suke ihu, wasu kuma sun toshe tituna lamarin da ya sa ƴansanda suka harba hayaƙi mai sa hawaye domin tarwatsa masu zanga-zangar.

    A cewar masu zanga-zangar, cibiyar na iya jefa rayukan mutanen ganin cikin haɗari da kuma yiwuwar ɓarkewar cutar.

    Joyce Wangui, wata mazauniyar Nanyuki ta ce "abin takaici ne yadda gwamnati ta nuna rashin damuwarta game da lafiyar ƴaƴanmu da al'ummarmu. Ba ma son a gina wannan cibiya a Laikipia."

    Marlin Ndegwa, wani shugaban al'ummar yankin ya ce masu zanga-zangar sun ɗauki matakin ne domin su nuna rashin goyon bayansu ga gina cibiyar Ebola a garin.

    A makon da ya gabata ne wata kotun Kenya ta dakatar da shirin Amurka na buɗe cibiyar killace masu Ebola ta Amurkawa a ƙasar. Lamarin dai ya janyo cece-kuce da kuma damuwa a tsakanin jama'a.

    Zuwa yanzu ba a samu ɓullar Ebola a Kenya ba sai dai ma'aikatar lafiya ta kafa cibiyar kula da kuma killace masu cutar a sassan ƙasar.

  20. Ƴansanda sun yi gargaɗi game da harin martani kan ƴan Afirka ta Kudu

    ..

    Asalin hoton, AFP via Getty Images

    Ƴansanda a Najeriya sun yi gargaɗi kan kai hare-haren ramuwar gayya kan ƴan Afirka ta Kudu ko ma wuraren kasuwancinsu sakamakon zanga-zangar ƙin jinin baƙi da ake yi a Afirka ta Kudun.

    Ƴansanda sun buƙaci ƴan Najeriya da kada su ɗauki doka a hannunsu bayan "rahotannin hare-hare kan ƴan Najeriya a Afirka ta Kudu".

    Ba a samu rahoton faruwar irin hare-haren ba amma gargaɗin na zuwa ne bayan wani taron manyan jami'an tsaro.

    Ƴansandan Afirka ta Kudu ba su tabbatar da hare-hare kan baƙi ba duk da cewa gwamnati ta yi allawaai da miyagun laifukan da ake aikatawa kan baƙi.

    A baya-bayan nan ana ta zaman ɗar-ɗar a Afirka ta Kudu sakamakon zanga-zangar neman a tsaurara matakai kan baƙin haure.

    Ƙasashen Afirka da dama sun shawarci al'umominsu da su kasance cikin shirin ko ta kwana, inda a baya-bayan nan Ghana ta kwashe ɗaruruwan ƴan ƙasarta saboda tabbatar da tsaronsu.