KAI TSAYE, Yaƙin Iran da sauran abubuwan da ke faruwa a sassan duniya

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran yaƙin Iran da sauran abubuwan da ke faruwa a sassan duniya, Talata 05/05/2026

Rahoto kai-tsaye

Haruna Ibrahim Kakangi da Aisha Aliyu Jaafar da Abdullahi Bello Diginza

  1. Ƴan majalisar wakilan Najeriya 16 sun koma jam'iyyar NDC

    Majalisar wakilan Najeriya

    Asalin hoton, OTHER

    Aƙalla ƴan majalisar wakilan Najeriya 16 ne suka koma sabuwar jam'iyyar NDC, bayan ficewa daga jam'iyyar ADC.

    An sanar da sauya sheƙar ƴan majalisar ne a zaman majalisa na yau Talata.

    Ɗaya cikin ƴan majalisar da suka sauya shekar, Mukhtari Yarima da ke wakiltar Tarauni a jihar Kano, ya tabbatar wa da BBC.

    A ranar Lahadin da ta gabata ne dai jiga-jigan adawar ƙasar biyu, Peter Obi da Kwankwaso suka sanar da sauya sheƙa daga jam'iyyar ADC zuwa NDC.

    Tun bayan ficewar ƴan siyasar biyu ne dai magoya bayansu ke tururuwar shiga sabuwar jamiyyar.

  2. Shugaban Kamaru ya ƙara wa'adin kansilolin ƙananan hukumomin ƙasar

    Biya

    Asalin hoton, Getty Images

    Shugaban ƙasar Kamaru Paul Biya, ya kara wa'adin kansilolin kananan hukumomi, bayan da majalisar dokokin ƙasar ta ba shi ikon yin hakan a kwanakin baya.

    Matakin na nufin za a iya jinkirta zaɓen ƙananan hukumomi har zuwa watan Fabrairun baɗi.

    Wannan matakin na zuwa ne bayan da shugaban ƙasar ya tsawaita wa'adin ƴan majalisar dokoki zuwa watan Disamban shekarar da muke ciki bisa iƙirarin da gwamnatin ta yi na cewa ba ta da kuɗaɗen gudanar da zaɓen ƙananan hukumomin da na yan majalisar.

    A hukumance an tsara gudanar da zaɓukan ne a bara, tare da na shugaban ƙasa da na yankuna.

    Sai dai gwamnatin mista Biya ta jinkirta zaben zuwa shekarar da muke ciki domin ta rage ayyukan hukumar zaɓ e da kuma rage kuɗin da gwamnati ke kashewa.

    Sai dai ƴan hamayya na ganin wannan wata dabara ce da jamiyyar CPDM mai mulki ke son amfani da ita domin ta cigaba da mulki da kuma hana wasu yan siyasa tsayawa takara.

    A baya dokar zaɓen ta ba shugaban ƙasa damar tsawaita wa'adin kansiloli har tsawon watanni 18, sai dai kundin tsarin mulkin da aka yi wa gyaran fuska ya cire wa'adin kuma ya bashi damar tsawaita wa'adin har lokacin da yake so.

    Wasu dai na ganin an jinkirta zaɓukan kananan hukumomi da yan majalisar dokokin ne da nufin kaucewa yiwuwar rasa kujerun jamiyya mai mulki, a dai dai lokacin da yan adawa ke kara ƙarfi.

  3. Fira ministan Pakistan ya yi Allahwadai da harin Iran kan UAE

    Shehbaz

    Asalin hoton, Getty Images

    Fira ministan Pakistan Shehbaz Sharif, wanda ya kasance mai shiga tsakanin Amurka da Iran, ya ce ƙasarsa ta yi Allah wadai da babbar murya da hare haren makamai masu linzami da jirage maras matuƙa da Iran ta kai kan kayyayakin more rayuwa a Haɗaɗɗiyar daular larabawa a daren jiya.''

    Kamar yadda rahotanni suka bayyana, UAE ta ce ta kakkabo makamai masu linzami da jirage marasa matuƙa da dama a jiya Litinin, sai dai harin ya faɗa kan wata tashar samar da man fetir.

    A wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na sada zumunta, Sharif ya ce '' yana da matuƙar muhimmanci a mutunta yarjejeniyar tsagaita wutar da aka cimma, domin ya bayar da damar yin tattaunawar diflomasiyya da za ta kai ga samar da zaman lafiya da daidaito a yankin.''

    Pakistan ɗin ta kuma ce har yanzu tana musayar bayanai tsakanin ɓangarorin biyu, tare da samar da damarmakin da za su ƙarfafa wa ɓangarorin yarda da juna, sai dai a cewar ta musayar wuta makamancin na jiya na dagula lissafi.

  4. Sudan ta zargi Ethiopia da Haɗaɗɗiyar daular Larabawa da kitsa kai mata hari

    Al Burhan

    Asalin hoton, AFP

    Bayanan hoto, Janar Abdel Fattah al-Burhan

    Sudan ta yi wa jakadanta da ke Ethiopia kiranye, bayan da ta zargi Addis Ababa da Haɗaddiyar daular Larabawa da kitsa kai hari da jirgi mara matuki kan filin jirgin sama na Khartoum.

    Zargin na zuwa ne bayan jerin wasu hare hare da jirage maras matuka da aka kai a jiya Litinin, waɗanda kuma suka shafi wasu sansanonin soji da ke Khartoum.

    Da safiyar yau Talata ne ministan harkokin wajen Sudan Moheiddin Salem sa kuma kakakin sojin ƙasar Asim Awad Abd al Wahab suka ce suna da shaidu masu karfi kan cewa an harbo jirage marasa matukan ne daga filin jirgin saman Bahir Dar da ke Ethiopia.

    Sai dai gwamnatin Ethiopia ta yi watsi da zarge zargen, inda tace basu da tushe balle makama.

    Gwamnatin ta ce ƙasashen Ethiopia da Sudan na da daɗɗaɗiyar tarihi, hakan ne ma yasa ta ƙi ta bayyana wasu manyan laifukan keta ƴancin iyakokinta da tsaron ƙasarta da wasu daga cikin masu yaƙin basasar Sudan ɗin suka yi.

    Daga ciki har da tallafawa mayaƙan sa kai na TPLF da kuɗaɗe da makamai da sojojin Sudan ke yi, wanda ke taimaka musu wajen yin kutse a yammacin Ethiopia.

  5. Mutum shida sun mutu a sabbin hare haren Rasha a Ukraine

    yadda gidaje suka lalace a ukraine bayan harin Rasha

    Asalin hoton, Reuters

    Hare haren Rasha da jirage marasa matuƙa da makamai masu linzami sun hallaka mutum biyar a yankin Poltava da ke tsakiyar Ukraine.

    Ma'aikata uku da masu aikin ceto biyu ne suka mutu a harin da aka kai wata cibiyar sarrafa iskar gas.

    Shugaba Zelensky ya ce ƙarin mutum ɗaya ya kuma mutu a wani harin cikin dare a yankin Kharkiv.

    Gwamnan yankin Leningrad na Rasha, Alexander Drozdenko, ya ce harin jirgi mara matuƙi ya tayar da gobara a wani yanki mai masana'antu da ke birnin Kirishi.

    Moscow ta ce na'urorinta na kare sararin samaniya sun lalata kusan jirage maras matuƙa ɗari uku cikin dare.

    Rasha da Ukraine sun ce za su tsagaita wuta don ƙashin kansu a kwanaki masu zuwa.

  6. Za a soma jigilar maniyyata aikin Hajjin bana na jihar Kano nan da mako guda

    Maniyyata aikin hajji suna shiga jirgi

    Asalin hoton, NAHCON

    Hukumar kula da jin ɗaɗin alhazai ta jihar Kano ta sanar da ranar 14 ga watan Mayun 2026 a matsayin ranar da za a soma jigilar maniyyata daga jihar zuwa Saudiya domin aikin hajjin 2026.

    A cikin wata sanarwa da kakakin hukumar Sulaiman A Dederi ya fitar, shugaban hukumar Abubakar Ibrahim Matawalle ya sanar da ranar ne a yayin rufe taron bita kan aikin Hajji da aka gudanar a makarantar koyar da larabci da ke Kano.

    Ya ce an sanya ranar ne bayan da hukumar alhazai ta ƙasar ta fitar da jadawalinta, inda ya ƙara da cewa an zaɓi kamfanin Max Air a matsayin wanda zai yi jigilar maniyyata na jihar.

    Matawalle ya kuma ce hukumarsa ta kammala duk wani shiri domin tabbatar da kwashe dukkaninsu lami lafiya.

    Hukumar ta kuma buƙaci maniyyatan su ci gaba da bitar karatun da aka yi musu domin su fahimci yadda za su gudanar da ibadar har ta kasance karɓaɓɓiya.

    Hakazalika an buƙace su da su tabbatar sun bi dokokin da Saudiyya da Najeriya suka gindaya kan gudanar da aikin Hajjin bana.

    A ranar Lahadin da ta gabata ne aka soma jigilar maniyyatan, inda aka soma da maniyyata 474 daga jihar Kogi waɗanda suka tashi daga filin jirgin saman Abuja, babban birnin Najeriya.

  7. Hare-haren Isra'ila a Lebanon sun yi sanadiyyar mutuwar mutum 110 cikin kwanaki 5

    masu makoki

    Asalin hoton, EPA

    Ma'aikatar lafiya ta ƙasar Lebanon ta ce hare-haren da Isra'ila ta kai sun yi sanadiyar mutuwar mutane dari da goma tun daga ranar Alhamis, duk da yarjejeniyar tsagaita wuta da aka cimma sama da makonni biyu da suka gabata.

    Ranar litinin na daya daga cikin ranaku mafi muni a ‘yan kwanakin nan, inda sojojin Isra’ila suka kashe mutane goma sha bakwai da suka hada da kananan yara biyu.

    Wakilin BBC ya ce A kudancin Lebanon, wannan tsagaita wuta a suna ne kawai, Isra'ila ta ci gaba da kai hare-hare ta sama a kowace rana.

    Isra'ila dai ta dage kan cewa kungiyar Hezbullah ta ke kai wa hari.

    Kamfanin dillancin labaran kasar Lebanon ya ruwaito cewa, sojojin kasar Isra’ila sun kai hare-hare ta sama kan wasu wurare sama da ashirin a kudancin kasar ta Lebanon a jiya litinin

  8. An sami fashewar wani abu a wata masana'anta da ke tsakiyar China

    ma'aikatan kashe gobara

    Asalin hoton, Getty Images

    Aƙalla mutane 26 ne suka mutu sakamakon fashewar wani abu a wata masana'anta da ke lardin Hunan tsakiyar kasar China.

    Jami’an ceto sun kwashe duk mutanen da ke da nisan kilomita uku daga wurin, bayan fashewar, wanda kuma ya jikkata sama da mutum sittin.

    Shugaba Xi Jinping ya yi kira da a gaggauta gudanar da bincike kan lamarin da kuma yin ƙokari matuƙa wajen gano mutanen da har yanzu ba a san inda suke ba.

    Wakiliyar BBC ta ce sama da ma'aikatan bayar da agajin gaggawa guda ɗari hudu da tamanin ne suke gudanar da aikin gano waɗanda suka maƙale a cikin ginin.

  9. Iran ta gargaɗi Amurka kan sake komawa yaƙi

    Abbas Aragchi

    Asalin hoton, Reuters

    Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya ce abubuwan da suka faru a Mashigar Hormuz na nuni da cewa matakan soji ba za su iya warware abin da ya kira "rikicin siyasa" ba, yayin da ake fargabar sake ɓarkewar yaƙi tsakanin kasarsa da Amurka.

    Araghchi ya kuma gargaɗi Amurka kan ta yi taka tsan-tsan, kuma kar ta bari masu mummunan fata su sake jefa ta cikin yaƙi.

    Shugaba Trump ya yi wa yunƙurin Amurka na taimaka wa jiragen ruwan kasuwanci wucewa ta Mashigar Hormuz laƙabi da "Project Freedom", amma Mista Araghchi ya ce a zahiri ba haka lamarin ya ke ba.

    Iran da Amurka sun yi musayar wuta a mashigar ruwan a jiya Litinin, inda daga baya Trump ya yi gargaɗin cewa Amurka za ta shafe Iran daga doron ƙasa idan har ta kai hari kan jiragen ruwan ƙasarta.

  10. Assalamu Alaikum

    Masu bin shafin BBC Hausa kai-tsaye barkanmu da safiyar Talata.

    A yau ma, za mu kawo muku labaran irin wainar da ake toyawa a sassan duniya, kama daga yaƙin Amurka da Isra'ila kan Iran, da abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

    Da fatan za ku kasance tare da mu.