KAI TSAYE, Abubuwa da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 04/08/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwa da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Talata 04 ga watan Agustan 2026.

Taƙaitattu

Tsallake Bidiyo ka ci gaba
  • xxx
  • xxx
  • Bola Tinubu
  • Senator Gaya
  • xxx
  • xxx
  • Zahra Buhari
  • xxx
  • Nigeria
  • xxx
  • Davido
  • xxx
  • Zanga-zanga a aAfirka ta Kudu
  • xxx
  • Ummulkhairi Aliyu

Rahoto kai-tsaye

Daga Aisha Babangida da Usman Minjibir

  1. Mun fasa kai hari kan wurare uku a Ukraine saboda ta nemi afuwa - Iran

    ....

    Asalin hoton, IRNA

    Iran ta ce ta shirya kai hari kan wurare uku a Ukraine bayan wani hari da aka kai wa jirgin kasuwancinta, amma daga baya ta dakatar da shirin bayan Ukraine ta nemi afuwa inda ta ce harin ba a yi shi da nufin tayar da rikici da Tehran ba.

    Babban mai ba wa jagoran Iran shawara kan harkokin soji, Mohsen Rezaei, ya ce bayan tattaunawar da aka yi tsakanin ministocin harkokin wajen ƙasashen biyu, Ukraine ta bayyana cewa harin wani ɓangare ne na yaƙinta da Rasha, ba da niyyarta ta kai wa ƙasar hari ba.

    Rezaei ya kuma yi iƙirarin cewa hare-haren jiragen sama marasa matuƙi da makamai masu linzami da Iran ta kai kan sansanonin Amurka sun taimaka wajen daƙile duk wani shirin farmakin da Amurka za ta iya kai wa.

    Game da mashigar Hormuz kuwa, ya ce Iran ba za ta amince da buɗe wata hanyar jiragen ruwa da ba ta ƙarƙashin ikonta ba, yana mai gargaɗin cewa za ta kai hari kan duk wani jirgin da ya bijirewa umarninta."

  2. Sojojin Najeriya 86 sun tafi aikin wanzar da zaman lafiya a Guinea-Bissau

    ....

    Asalin hoton, Getty Images

    Rundunar sojin Najeriya ta tura jami'ai 86 zuwa ƙasar Guinea-Bissau domin aikin wanzar da zaman lafiya na ƙungiyar ECOWAS

    Rundunar ta ce wannan matakin na nuna ci gaba da jajircewar da Najeriya ke yi wajen tallafa wa zaman lafiya da tsaro a yankin Afirka ta Yamma.

    A wata sanarwa da rundunar sojin ta wallafa a shafukanta na sada zumunta, ta ce jami'an da aka tura sun tashi daga filin jirgin saman ƙasar da ke Abuja kuma sun isa Guinea-Bissau lafiya domin fara aikinsu ƙarƙashin umarnin ECOWAS.

    Rundunar ta kuma ce Najeriya na ci gaba da kasancewa cikin ƙasashen Afirka da suka fi bayar da gudunmawa wajen ayyukan wanzar da zaman lafiya na ECOWAS da Tarayyar Afirka da kuma Majalisar Ɗinkin Duniya.

    Rundunar sojin Najeriya dai ta ce wannan sabon aikin ya nuna muhimmiyar rawar da Najeriya ke takawa wajen hana rikice-rikice, gina zaman lafiya da kuma dawo da kwanciyar hankali a ƙasashen Afirka.

    An dai kafa wannan rundunar ne domin tallafa wa ɓangaren tsaro da kuma inganta yanayin siyasa a Guinea-Bissau, bayan shekaru ana fama da rikice-rikicen siyasa da juyin mulkin soja.

    Najeriya dai ta daɗe tana cikin ƙasashen da suka fi tura sojoji zuwa ayyukan ECOWAS, inda ta bayar da dakaru, kayan aiki da jagoranci a ƙasashe irin su Liberiya, Saliyo, Gambiya da kuma Guinea-Bissau.

    Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da Najeriya ke fuskantar ƙalubalen tsaro a sassa daban-daban na ƙasar da suka haɗa da hare-haren 'yanbindiga, satar mutane domin neman kuɗin fansa da dai sauransu.

  3. Iran ta ƙaryata iƙirarin dake cewa shugaban ƙasar Pezeshkian ya yi murabus

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Wani babban jami'i a ofishin Shugaban Iran ya bayyana rahotannin da ke cewa shugaban ƙasar, Massoud Pezeshkian ya yi murabus a matsayin “karya tsagwaronta.”

    Mehdi Tabatabaei, mataimakin daraktan sadarwa da yaɗa bayanai na ofishin shugaban ƙasar, ya ce wasu masu tsattsauran ra'ayi ne ke yaɗa ƙarya domin kawo cikas ga haɗin kan ƙasa.

    Tun da farko, wasu kalamai da malamin addini Mohammad Bagher Kharrazi ya yi sun bazu sosai a kafafen yaɗa labarai da sada zumunta a Iran.

    Kharrazi ya yi iƙirarin cewa Mojtaba Khamenei ya ce idan Pezeshkian ya sake miƙa takardar murabus, za a amince da ita.

    Sai dai fadar shugaban ƙasar ta yi watsi da wannan iƙirari, tana mai cewa ba shi da tushe balle makama.

  4. Assalamu alaikum

    Jama'a barkanmu da wannan safiya ta Talata daga wannan shafin namu na BBC Hausa, inda za mu ci gaba da kawo muku labaran kai-tsaye na abubuwan da suke faruwa a Najeriya da sassan duniya.

    Aisha Babangida ce ke fatan sake kasancewa da ku a wannan lokaci.

    Za ku iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta na facebook da X da kuma whatsapp domin karanta wasu labaran da kallon bidiyo da ma tafka muhawara.

    Ku kasance tare da mu.