Rundunar sojin Najeriya ta tura jami'ai 86
zuwa ƙasar Guinea-Bissau domin aikin wanzar da zaman lafiya na ƙungiyar ECOWAS
Rundunar ta ce wannan matakin
na nuna ci gaba da jajircewar da Najeriya ke yi wajen tallafa wa zaman lafiya
da tsaro a yankin Afirka ta Yamma.
A wata sanarwa da rundunar sojin ta wallafa a
shafukanta na sada zumunta, ta ce jami'an da aka tura sun tashi daga filin
jirgin saman ƙasar da ke Abuja kuma sun isa Guinea-Bissau lafiya domin fara aikinsu ƙarƙashin umarnin ECOWAS.
Rundunar ta kuma ce Najeriya na ci gaba da
kasancewa cikin ƙasashen Afirka da suka fi bayar da gudunmawa wajen ayyukan
wanzar da zaman lafiya na ECOWAS da Tarayyar Afirka da kuma Majalisar Ɗinkin
Duniya.
Rundunar sojin Najeriya
dai ta ce wannan sabon aikin ya nuna muhimmiyar rawar da Najeriya ke takawa
wajen hana rikice-rikice, gina zaman lafiya da kuma dawo da kwanciyar hankali a
ƙasashen Afirka.
An dai kafa wannan
rundunar ne domin tallafa wa ɓangaren tsaro da kuma inganta yanayin siyasa a
Guinea-Bissau, bayan shekaru ana fama da rikice-rikicen siyasa da juyin mulkin
soja.
Najeriya dai ta daɗe
tana cikin ƙasashen da suka fi tura sojoji zuwa ayyukan ECOWAS, inda ta bayar
da dakaru, kayan aiki da jagoranci a ƙasashe irin su Liberiya, Saliyo, Gambiya
da kuma Guinea-Bissau.
Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da Najeriya ke fuskantar ƙalubalen tsaro a sassa daban-daban na ƙasar da suka haɗa da hare-haren 'yanbindiga, satar mutane domin neman kuɗin fansa da dai sauransu.