Yadda aka yi sulhu tsakanin Barau Jibrin da Abdullahi Gwarzo

Asalin hoton, Aliyu Samba/Facebook
Alamu na nuna cewa an daƙile faruwar wani ɓangare na rikicin da ke ƙoƙarin ruruwa a jam'iyyar APC reshen jihar Kano da ka iya jefa jam'iyyar cikin wani hali na rashin tabbas.
Rikicin dai ya kunno kai ne tsakanin mataimakin shugaban majalisar dattawa, Barau Jibrin da tsohon mataimakin gwamnan jihar Kano kuma tsohon ƙaramin ministan gidaje na Najeriya, Abdullahi Tijjani Muhammad Gwarzo kan takarar majalisar dattawa a yankin Kano ta Arewa.
Ana dai alakanta rikicin da daɗaɗɗe wanda yake rikiɗa sakamakon al'amuran siyasa da suka faru a baya-bayan.











