EFCC ta gurfanar da wanda ake zargi da damfarar maniyyata aikin Hajji

Asalin hoton, EFCC/Facebook
Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa a Najeriya EFCC ta gurfanar da wani mutum a gaban wata babbar kotun jihar Oyo bisa zargin shi da damfarar maniyyata ikin hajji naira miliyan 56.4.
An gurfanar da mutumin ne kan zarge-zarge 57 wadanda ke da alaƙa da fashi da kuma yaudara.
Hukumar ta lissafo sunayen wasu mutane 10 wadanda ta ce mutumin da take zargi ya damfara.
Bayanin shari’ar da EFCC ta shigar ya nuna cewa mutumin ya karɓi kuɗin naira miliyan 56,491,000 daga mutane daga watan Nuwamban 2022 zuwa watan Yulin 2024.
Mutumin ya riƙa shaida wa mutanen da yake karɓar kudi daga wurin su cewa shi jami’in hukumar kula da mahajjata ne ta jihar Kaduna.
EFCC ta ce ya karɓi kuɗaɗen a hannunsu ne bisa hujjar cewa zai taimaka musu wajen tsara tafiyarsu zuwa aikin hajjin shekarar 2023.
Hukumar ta ƙara da cewa mutumin ya ba su rasiɗin shaidar biyan kuɗi na ƙarya daga jihar Kaduna da kuma ƙasar Saudiyya.




















