Kotu ta yanke wa ɗan’uwan tsohon shugaban Syria, Assad hukuncin kisa
Wata Kotu a Syria ta yankewa ɗanuwan tsohon shugaban ƙasar, Bashar al-Assad hukuncin kisa bayan samunsa da tafaka laifukan yaƙi da kuma cin zarafin ɗan adam.
An kama Wassim al-Assad a watan Yuni bara.
Mutane da dama na danganta shi da ƙungiyoyin fataucin miyagun ƙwayoyi , sai dai kotu ta ce bata same shi da laifi ba saboda rashin shaida.
Hakuncin ya zo mako guda bayan yankewa Bashar al-Assad hukuncin kisa yayin da ya ke ci gabad a gudun hijira a Rasha.
Ana ganin matakin a matsayin kokarin Siriya na yin adalci bayan kwashe shekaru ana gwabza rikici.