Isra'ila ta kashe mayaƙan Hezbollah bakwai a Lebanon

Asalin hoton, Getty Images
Rundunar sojin Isra'ila ta ce sun kashe mayaƙan Hezbollah bakwai a kudancin Lebanon.
A cikin wata sanarwa da rundinar sojojin ta wallafa a shafukan sada zumunta, ta ce mutanen da aka kashe sun kasance suna jigilar makamai da alburusai ga Hezbollah "a kusa da sojojin Isra'ila da ke yankin Ha'il" a kudancin Lebanon.
A wani bidiyo da sojojin Isra'ila suka fitar tare da sanarwar, an ga wasu mutane na sauke buhuna da dama daga cikin wata mota, sannan suka shigar da su cikin wani gini.
Rundinar Sojin Isra'ilar ta ce buhunan na ɗauke da makamai.
Sanarwar ta ce ginin yana yankin Mansala da ke lardin Dakahlia, kuma ana amfani da shi a matsayin "sansanin soja da cibiyar bayar da umarni."
Har wa yau sanarwar ta rawaito, Rundinar sojojin na jaddada cewa za su ci gaba da kai hare-harensu domin "kawar da barazanar" da ke fuskantar ƙasarsu.



































