Kashi 87 cikin 100 na matalautan Najeriya a Arewa suke - Bankin Duniya

Mabarata

Asalin hoton, Getty Images

An wallafa

Wani rahoto da Babban Bankin Duniya ya fitar ya nuna cewa kashi 87 cikin 100 na matalautan da ke Najeriya suna zaune ne a arewacin kasar.

Rahoton ya ce talauci a yankin kudu maso kudancin kasar ya yi gagarumar raguwa tsakanin 2011 da 2016.

A ranar Litinin ne Bankin Duniyar ya fitar da rahoton.

"Talaucin da ake fama da shi a arewacin kasar musamman a arewa maso yammaci yana ci gaba da karuwa.

''Kusan rabin matalautan mutane suna zaune ne a arewa maso yamma kuma kashi 87 na matalautan kasar na zaune ne a arewacin kasar," a cewar rahoton.

Rahoton ya kara da cewa: "Talaucin da ake fama da shi a kudancin kasar bai wuce kashi 12 cikin 100 ba inda ake samun bambanci tsakanin yankunan da ke kudancin kasar.

''An samu raguwar talauci a yankin tsakanin 2011-2016."

A yanzu dai kason yawan mataulatan da ke Najeriya ya zarce na Indiya, kamar yadda rahoton ya zayyana.